Subscribe Our Channel

 CIKAKKEN SHARHIN HADISIN BIYAYYA GA SHUWAGABANNI : 

Shekara shida da suka wuce mun ta'ba yin sharhi ga shahararren Hadisin nan ; Hadisin Al'irbad bin Sãriya , ta hanyar fito da wasu fa'idoji da Hadisin ya 'kunsa ta 'bangaren hani game da bidi'a da kuma hukuncin ta a cikin Addini .

A yau _ in Allah ya yarda _ zamu yi magana ne akan ga'ba ɗaya daga cikin ga'bo'bin hadisin wacce take magana akan wajibcin biyayya ga shuwagabanni .

Ga nassin ga'bar Hadisin :

" ﺃﻭﺻﻴﻜﻢ ﺑﺘﻘﻮﻯ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﺰ ﻭ ﺟﻞ ، ﻭﺍﻟﺴﻤﻊ ﻭ ﺍﻟﻄﺎﻋﺔ ، ﻭﺇﻥ ﺗﺄﻣﺮ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻋﺒﺪ "

‏( ﺃﺑﻮ ﺩﺍﻭﺩ : ٤٦٠٧ ، ﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ : ٢٦٧٦، ﺍﺑﻦ ﻣﺎﺟﻪ : ٤٢ )

Zamu fitar da fa'idojin da wannan ga'bar ta 'kunsa ta hanyoyi kamar haka :

1. wannan hadisin yana nuna wajibcin biyayya ga Shuwagabanni a duk yanda suke ; ma'ana shin nagartattu ne su ko ko Azzalmai ne marasa adalci .

Saboda lafazin " ﺍﻟﺴﻤﻊ ﻭﺍﻟﻄﺎﻋﺔ " da su ka zo a cikin hadisin lafuzza wa'danda suke masdarai ( ﻣﺼﺪﺭ ) kuma tattare da su akwai 'kamshin fi'ili , ma'ana zasu yi aikin da fi'ilansu suke yi ; ko dai yiwa fa'ili ruf'a ( ﺭﻓﻊ ﺍﻟﻔﺎﻋﻞ ), ko kuma yiwa maf'uli Nasba ( ﻧﺼﺐ ﺍﻟﻤﻔﻌﻮﻝ ) , bisa gwargwadon 'dabi'ar fi'illan su na samarwassu ga maf'uli ko ta'kaituwarsu ga fa'ili ( ﺍﻟﻠﺰﻭﻡ ﻭﺍﻟﺘﻌﺪﻱ ) .

To su wa'dannan lafuzza anan asalin fi'illansu suna samar da maf'uli , ta'kadirin jumlar idan an maida kalmomin zuwa fi'illansu shine kamar haka :

" ﻭﺃﻥ ﺗﺴﻤﻌﻮﺍ ﻭ ﺗﻄﻴﻌﻮﺍ ﺃﻣﺮﺍﺀﻛﻢ "

Saboda haka , tuddan dai fi'illan kalmomin 'dabi'ar su itace Samar da maf'uli ( ﺍﻟﺘﻌﺪﻱ ) , to haka ma ya kamata masdarin su su zama matu'kar masdaran sun cika sharu'd'dan haka , to kuma anan wa'dannan masdarai sun cika sharu'd'dan saboda fi'ili tare da harafin " An " ( ﺃﻥ ) suna yiwuwa su zauna a makwafin masdaran , kuma a lafazin su na masdari suna 'dauke da harafin "Alif da lamun " ( ﺍﻝ) , wanda kuma siffantuwar masdari da wa'dannan sifofi yana daga cikin fuskar da take halasta gudanar da magudanar fi'ilin sa .

Ibnu Malik ya ce :

ﺑﻔﻌﻠﻪ ﺍﻟﻤﺼﺪﺭ ﺃﻟﺤﻖ ﻓﻲ ﺍﻟﻌﻤﻞ * * ﻣﻀﺎﻓﺎ ﺃﻭ ﻣﺠﺮﺩﺍ ﺃﻭ ﻣﻊ ﺍﻝ .

ﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﻓﻌﻞ ﻣﻊ ﺃﻥ ﺃﻭ ﻣﺎ ﻳﺤﻞ * * ﻣﺤﻠﻬﺎ ﻭ ﻻﺳﻢ ﻣﺼﺪﺭ ﻋﻤﻞ .

To idan muka fahimci wannan sai muga a lafazin Hadisin Annabi bai fa'di maf'uli ba ga wa'dannan lafuzza , sai ya ce :

" ﻭﺍﻟﺴﻤﻊ ﻭ ﺍﻟﻄﺎﻋﺔ ﻭ ﺇﻥ ﺗﺄﻣﺮ ﻋﻠﻴﻜﻢ ..."

Rashin ambaton abunda ke da ala'ka da wa'dannan lafuzza anan yana nuni akan fa'idoji biyu _ a iya abunda muka iya hararowa _ a wurin malaman Balaga :

* Ba'a ambaci Kalmar da take ala'kantuwa da Masdarin bane saboda an ambaci lafazin da yake fayyace ha'ki'kaninsa a cikin zancen da ya biyo baya ; inda Annabi ya ce :

" ﻭ ﺇﻥ ﺗﺄﻣﺮ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻋﺒﺪ "

Kenan wannan lafazin yana fayyace ibhamin da aka yi wurin rashin fayyace ha'ki'kanin maf'uli wanda yake ratayuwa ga wa'dannan masdarai guda biyu .

Ta'kadirin jumlar sai ya zama kamar haka :

" ﻭﺍﻟﺴﻤﻊ ﻭﺍﻟﻄﺎﻋﺔ ﻟﻸﻣﺮﺍﺀ ﻭﺇﻥ ﺗﺄﻣﺮ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻋﺒﺪ "

irin wannan salon zancen ya zo a cikin Al'kur'ani , inda Allah yake cewa :

" ﻭ ﻟﻮ ﺷﺎﺀ ﻟﻬﺪﺍﻛﻢ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ "

Anan Allah bai ambaci maf'ulin fi'ilin " ﺷﺎﺀ " ba , saboda lafazin da ya zo baya ya fayyace shi " ﻟﻬﺪﺍﻛﻢ "

Ta'kadirin Ayar sai ya zama :

" ﻭﻟﻮ ﺷﺎﺀ ﻫﺪﺍﻳﺘﻜﻢ ﻟﻬﺪﺍﻛﻢ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ "

zuwa da zance a bisa irin wannan salo yana daga cikin dalilan da suke sa a goge maf'uli ga Kalmar da take da bu'katuwa zuwa gare shi a wurin malaman Balaga .

Ibnu Shihnah Alhalaby yana bayanin dalilan da suke hukunta

share maf'uli ga fi'ili sai yake cewa :

" ﻭ ﺍﻟﺤﺬﻑ ﻟﻠﺒﻴﺎﻥ ﻓﻴﻤﺎ ﺃﺑﻬﻤﺎ ** ﺃﻭ ﻟﻤﺠﻲﺀ ﺍﻟﺬﻛﺮ ﺃﻭ ﻟﺮﺩ .

* Fa'idar goge maf'ulin shine gamewa ( ﺍﻟﺘﻌﻤﻴﻢ ) ; wato

umurni da biyayya ya game dukkan nau'ukan shuwagabanni ;

sawa'un Adilai ne ko Azzalumai , Musulmi ne ko kafiri .

Bisa

haka sai mu fitar da Natija kamar haka :


* wajibi ne biyayya ga shugaba a duk yanda yake ; Musulmi

ne ko kafiri , Adali , ko Azzalumi , saboda daga cikin fa'idojin

share maf'uli a wurin malaman Balaga akwai fa'idantar da

game hukunci .

Ibnu Shihnah yana cewa acikin littafin sa " ﻣﺄﺓ ﺍﻟﻤﻌﺎﻧﻲ ﻭ ﺍﻟﺒﻴﺎﻥ

" game da fa'idojin share maf'uli :


" ﺃﻭ ﻫﻮ ﻟﻠﺘﻌﻤﻴﻢ ﺃﻭ ﻟﻠﻔﺎﺻﻠﺔ * * ﺃﻭ ﻫﻮ ﻻﺳﺘﻬﺠﺎﻧﻚ ﺍﻟﻤﻘﺎﺑﻠﺔ .

Don haka babu wanda ya halatta a wareshi daga wannan

gamammen sa'ko na umurni da biyayya ga ko wane irin

shugaba sai wanda dalili ya ware shi ya haramta biyayya

gareshi .

wanda dalili na shari'a ya wareshi kuwa shine shugaba Kafiri ,

shi baya halatta ayi masa biyayya matu'kar Kafircin sa ya

tabbata , wajibine ma a sauke shi daga shugabancin matu'kar

akwai iko akan haka .

Hadisin Ubadah bin Samit shine ya ke'bance kafirin shugaba

daga rashin wajibcin yi masa biyayya , inda Annabi yake

cewa :

" ﺇﻻ ﺃﻥ ﺗﺮﻭﺍ ﻛﻔﺮﺍ ﺑﻮﺍﺣﺎ ﻋﻨﺪﻛﻢ ﻣﻦ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻴﻪ ﺑﺮﻫﺎﻥ "

( ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ : ٧٠٥٦ )


Saboda haka Adalin shugaba Musulmi da Azzalumi dukkan su

suna nan cikin gamammen umurnin Annabi na biyayya ga

shuwagabanni , musamman ma an samu wasu hadisai

tabbatattu da suka 'kara tabbatar da biyayya ga Azzaluman

Shuwagabanni a ke'be , kamar Hadisin Ibnu Mas'ud inda

Annabi yake cewa :


" ﺇﻧﻜﻢ ﺳﺘﺮﻭﻥ ﺑﻌﺪﻱ ﺃﺛﺮﺓ ، ﻭ ﺃﻣﻮﺭﺍ ﺗﻨﻜﺮﻭﻧﻬﺎ " . ﻗﺎﻟﻮﺍ : ﻓﻤﺎ ﺗﺄﻣﺮﻧﺎ ﻳﺎ

ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ؟ ﻗﺎﻝ : " ﺃﺩﻭﺍ ﺇﻟﻴﻬﻢ ﺣﻘﻜﻢ ﻭ ﺳﻠﻮﺍ ﺍﻟﻠﻪ ﺣﻘﻜﻢ "

( ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ : ٧٠٥٢ )


2. lafzin " ﻭ ﺇﻥ ﺗﺄﻣﺮ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻋﺒﺪ " Shi lafazin " ﺇﻥ " yana nuni ne

akan rashin tabbatuwar aikin da aka sanya shi a matsayin

shara'di , ko kuma 'karancin sa .

kenan ma'anar jumlar itace kamar haka :

" ko da ta yiwu wani wula'kantaccen Bawa ya shugabantu

akan Ku duk da cewa hakan yana da wahalar aukuwa , to

idan hakan ya auku Ku yi masa biyayya "

wannan shine Asalin ma'anar da lafazin yake nuni zuwa gare

shi a wurin malaman Balaga ,akasin sa shine lafazin " ﺇﺫﺍ " ;

shi yana fa'idantar da tabbacin faruwàn aiki da yawaituwar

Sa , shi yasa galibi fi'ilin da yake zuwa bayansa a matsayin

shara'di yake zuwa a sura ta Aikin da ya gabata ( ﺍﻟﻔﻌﻞ

ﺍﻟﻤﺎﺿﻲ ) , domin ishara zuwa ga tabbacin samuwan shara'din

kamar kace gashinan a auke , sa'banin lafazin " ﺇﻥ " ; wanda

shi Galibi shara'din sa yakan zo a sura ta mudari'i , domin

ishara zuwa ga rashin tabbas wurin samuwar sa .

Misalin wannan Acikin Alqur'ani shine fa'din Allah ma'daukaki

:


" ﻭﺇﺫﺍ ﺃﺫﻗﻨﺎ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﺭﺣﻤﺔ ﻓﺮﺣﻮﺍ ﺑﻬﺎ "

Anan da yake rahamar Allah tana da yalwa kuma bata rabuwa

da mutane a kowane lokaci , sai Allah ya yi Amfani da lafazin

" ﺇﺫﺍ " domin nuni zuwa ga tabbacin samuwar rahamar ga

mutane da yawaitar rahamar , shi yasa maf'ulin yazo a siga

ta " Nakirah" ; wacce take nuni akan yawaituwa ( ﺍﻟﺘﻜﺜﻴﺮ ).


Amma da Allah zai yi magana akan kishiyar rahamar _ wacce

take qanqanuwa ce idin aka dangantata da Rahama _ sai ya

ce :


" ﻭ ﺇﻥ ﺗﺼﺒﻬﻢ ﺳﻴﺌﺔ ..."


Anan sai ya yi amfani da lafazin " ﺇﻥ " domin ishara zuwa ga

qarancin samuwar musiba ga mutane idan aka kwatanta da

samuwar rahama , shi yasa ma aka zo da fa'ilin " ﺳﻴﺌﺔ " a

sura ta "NAKIRAH" ; wacce anan take nuni akan 'karanci

" ( ﺍﻟﺘﻘﻠﻴﻞ ).


Al'imamu Assuyu'dy ya yi bayanin ma'anonin wa'dannan

lafuzza _a wurin malaman Balaga _ a cikin Alfiyyar sa ta

Balaga , inda yake cewa :


" ﻓﻐﻴﺮ ﻟﻮ ﻟﻠﺸﺮﻁ ﻓﻲ ﺍﺳﺘﻘﺒﺎﻝ *** ﻟﻜﻦ ﺇﻥ ﺗﺨﺘﺺ ﺑﺎ ﻟﻤﺤﺎﻝ .

ﻟﻜﻮﻧﻬﺎ ﻓﻲ ﺍﻷﺻﻞ ﻟﻠﺬﻱ ﻋﺪﻡ *** ﺟﺰﻣﺎ ﻭ ﻋﻜﺴﻬﺎ ﺇﺫﺍ ﻣﻦ ﺛﻢ ﻋﻢ "


Saboda haka anan Annabi yana umurni ne da biyayya ga

shugaba koda kuwa shugabancin nasa ya samu ne ta wata

irin hanya wacce take baquwa ga mutane .


3. Umurni da ya zo a wannan Hadisi na biyayya ga shugaba

ya zo ne a sake ( ﻣﻄﻠﻖ ) ، wato umurni da biyayya gareshi a

kowane hali ; biyayya gareshi akan aikin 'da'a da aikin sa'bo .

Amma wasu hadisai sun iyakance 'da'ar da za'a yi masa ;

cewa 'da'a ce a cikin abundà bai sa'bawa shari'a ba .


Hadisin Abdullah bin Mas'ud yana tabbatar da wannan , inda

Annabi yake cewa :


" ﺍﻟﺴﻤﻊ ﻭ ﺍﻟﻄﺎﻋﺔ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻤﺮﺀ ﺍﻟﻤﺴﻠﻢ ﻓﻴﻤﺎ ﺃﺣﺐ ﻭ ﻛﺮﻩ ﻣﺎ ﻟﻢ ﻳﺆﻣﺮ

ﺑﻤﻌﺼﻴﺔ ، ﻓﺈﺫﺍ ﺃﻣﺮ ﺑﻤﻌﺼﻴﺔ ﻓﻼ ﺳﻤﻊ ﻭ ﻻ ﻃﺎﻋﺔ "


( ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ : ٧١٤٤ )


Acikin wannan akwai martani ga 'kungiyoyin bidi'a na

Mu'tazila da Khawarij wa'danda suke halatta tawaye ga

shugaba akan sa'bo , hakanan akwai martani ga wasu jama'a

da suka bayyana a tarihi , wa'danda ake musu laqabi da "

ALMARWANIYYAH " wa'danda suke ganin ana yiwa shugaba

biyayya acikin komai !! , da kuma Qungiyar Shi'a Rafidha ;

wa'danda suke ganin wajibcin biyayya ga limamansu acikin

dukkan komai .

Saboda Annabi bai saryar da biyayya ba ga shugaba gaba

'daya saboda ya yi umurni da sa'banin shari'a , a'a sai ya

wajabta biyayya gareshi a inda bai sa'ba da shari'a ba , kuma

ya haramta hakan a inda ya sa'bawa shari'ah.

Wannan matsakaiciyar matsaya itace mazhabar Ahlussunnati

waljama'a gameda biyayya ga shuwagabanni , Shaikhul Islam

yana cewa :


" ﺇﻧﻬﻢ ‏( ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺴﻨﺔ ‏) ﻻ ﻳﺠﻮﺯﻭﻥ ﻃﺎﻋﺔ ﺍﻹﻣﺎﻡ ﻓﻲ ﻛﻞ ﻣﺎ ﻳﺄﻣﺮ ﺑﻪ ، ﺑﻞ

ﻻ ﻳﻮﺟﺒﻮﻥ ﻃﺎﻋﺘﻪ ﺇﻻ ﻓﻴﻤﺎ ﺗﺴﻮﻍ ﻃﺎﻋﺘﻪ ﻓﻴﻪ ﺍﻟﺸﺮﻳﻌﺔ ، ﻓﻼ ﻳﺠﻮﺯﻭﻥ

ﻃﺎﻋﺘﻪ ﻓﻲ ﻣﻌﺼﻴﺔ ﺍﻟﻠﻪ ﻭ ﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﺇﻣﺎﻣﺎ ﻋﺎﺩﻻ "

( ﻣﻨﻬﺎﺝ ﺍﻟﺴﻨﺔ ، ٤ /٨٦ )


4. lafazin " ﺗﺄﻣﺮ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻋﺒﺪ " , yana nuni akan wajibcin biyayya

ga shugaba koda kuwa shugaban ya shugabantu akan mutane

ne ta hanyar mur'kushe da 'karfin makami da tursasasu har

ya haye kan madafan iko .

Abunda yake tabbatar da wannan ma'anar shine lafazin " ﺗﺄﻣﺮ

" , saboda ma'aunin lafazin a ilimin sarfu shine " ﺗﻔﻌّﻞ" , shi

kuma wannan wazani daga cikin ma'anoninsa a wurin

malaman sarfu akwai : " ﺍﻟﺘﻜﻠﻒ " , ma'ana zagewa da

jajaircewa akan cimma wani abu .

Kenan wannan lafazin yana tabbatar da wajibcin biyayya ga

wanda ya dafe madafan iko koda kuwa hakan ya yiwu gareshi

ne tahanyar sanya 'karfi da mur'kushe mutane har ya cimma

zama shugaba akansu .

Babu shakka matu'kar mutum ya iya mur'kushe mutane da

'karfi alokacin da babu mulki tattare da shi , to idan har ya

kai ga ya dafe madafan iko akansu , babu shakka wa'dannan

mutane basu da wata maslaha garesu da ta wuce biyayya

gareshi . Saboda matu'kar basu iya nasara akan shi ba Kafin

ya zama shugaba to babu yanda zasu iya da shi bayan ya

zama shugaba akansu .


Wannan ya sa Mazhabar Magabata ta gudana akan tabbatar

da abunda wannan lafazi yake hukuntawa ; na wajibcin

biyayya da haramcin tawaye ga Shugaban da ya haye

madafan iko ta hanyar 'karfin makami , Al'imam Ahmad bin

Hanbal ya ce :


" ﻭ ﺍﻟﺴﻤﻊ ﻭﺍﻟﻄﺎﻋﺔ ﻟﻸﻳﻤﺔ ﻭ ﺃﻣﻴﺮ ﺍﻟﻤﺆﻣﻨﻴﻦ ؛ ﺍﻟﺒﺮ ﻭ ﺍﻟﻔﺎﺟﺮ ، ﻭﻣﻦ ﻭﻟﻲ

ﺍﻟﺨﻼﻓﺔ ، ﻭﺍﺟﺘﻤﻊ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻋﻠﻴﻪ ، ﻭ ﺭﺿﻮﺍ ﺑﻪ ، ﻭ ﻣﻦ ﻋﻠﻴﻬﻢ ﺑﺎ ﻟﺴﻴﻒ

ﺣﺘﻰ ﺻﺎﺭ ﺧﻠﻴﻔﺔ ﻭ ﺳﻤﻲ ﺃﻣﻴﺮ ﺍﻟﻤﺆﻣﻨﻴﻦ "


( ﺃﺻﻮﻝ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻟﻺﻣﺎﻡ ﺃﺣﻤﺪ ، ٧ )


Ibnu Ba'd'dal Almaliky ya hikaito ijma'in Malamai akan

tabbatar da ma'anar da wannan lafazi ya ke nunawa , yana

cewa :


" ﻭ ﻗﺪ ﺃﺟﻤﻊ ﺍﻟﻔﻘﻬﺎﺀ ﻋﻠﻰ ﺃﻥ ﺍﻹﻣﺎﻡ ﺍﻟﻤﺘﻐﻠﺐ ﺗﻠﺰﻡ ﻃﺎﻋﺘﻪ ﻓﻲ ﺍﻟﺠﻬﺎﺩ

ﻣﻌﻪ ﻭ ﺃﻥ ﻃﺎﻋﺘﻪ ﺧﻴﺮ ﻣﻦ ﺍﻟﺨﺮﻭﺝ ﻋﻠﻴﻪ ، ﻟﻤﺎ ﻓﻲ ﺫﻟﻚ ﻣﻦ ﺣﻘﻦ

ﺍﻟﺪﻣﺎﺀ "


( ﺣﺎﺷﻴﺔ ﺍﻟﺘﺎﻭﺩﻱ ﺑﻦ ﺳﻮﺩﺓ ﻋﻠﻰ ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ، ٦ / ٣٥٠ )


5. Lafazin " ﺗﺄﻣﺮ " yana iya nuni akan 'kulluwan Shugabancin

Shugaba ta hanyar shugabantarwar da masu wu'ka da Nama

a jagorancin mutane sukai masa ( ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺤﻞ ﻭ ﺍﻟﻌﻘﺪ ) , saboda

lafazin yana iya zama "MU'DAWI' " ne ( ﺍﻟﻤﻄﺎﻭﻉ ) na lafazin "

ﺃﻣّﺮ " , wanda hakan kuma yana daga cikin ma'anar ma'aunin

lafazin ( ﺗﻔﻌّﻞ) a Ilimin Sarfu .

Kenan ma'anar jumlar itace :


" koda masu fa'da _ aji daga cikinku sun shugabantar da

Bawa akanku , kuma bawan ya shugabantu , to Ku yi masa

biyayya "

Bisa wannan ma'anar , sai lafazin ya zama ya dace _ a

ma'ana _ da lafazin riwayar Bukhari daga hadisin Anas bin

Malik , inda Annabi yake cewa :


" ﺍﺳﻤﻌﻮﺍ ﻭ ﺃﻃﻴﻌﻮﺍ ﻭ ﺇﻥ ﺍﺳﺘﻌﻤﻞ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻋﺒﺪ ﺣﺒﺸﻲ ﮔﺄﻥ ﺭﺃﺳﻪ ﺯﺑﻴﺒﺔ

"

( ﺑﺨﺎﺭﻱ ، ٧١٤٢ )

Hakanan ma'anar lafazin ya dace da riwayar Muslim , daga

Hadisin Ummul Hasin , Annabi yake cewa :


" ﺍﺳﻤﻌﻮﺍ ﻭ ﺃﻃﻴﻌﻮﺍ ﻭ ﺇﻥ ﺃﻣﺮ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻋﺒﺪ ﺣﺒﺸﻲ ﻣﺠﺪﻉ "


Bisa wannan ma'anar , lafazin hadisin yana tabbatar da

wajibcin biyayya ga shugaba wanda masu fa'da _aji cikin

mutane suka shugabantar , koda kuwa mutane basa sonsa ,

kuma samuwan shugabanci ta wannan fuskar kar'ba'b'be ne a

shari'a . wannan shine mazhaba ta Ahlussunnah , Ibnu

Taimiyyah yana cewa :


" ﺍﻹﻣﺎﻣﺔ ﻋﻨﺪﻫﻢ ‏( ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺴﻨﺔ ‏) ﺗﺜﺒﺖ ﺑﻤﻮﺍﻓﻘﺔ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺸﻮﻛﺔ ﻋﻠﻴﻬﺎ ، ﻭﻻ

ﻳﺼﻴﺮ ﺍﻟﺮﺟﻞ ﺇﻣﺎﻣﺎ ﺣﺘﻰ ﻳﻮﺍﻓﻘﻪ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺸﻮﻛﺔ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﻳﺤﺼﻞ ﺑﻄﺎﻋﺘﻬﻢ

ﻟﻪ ﻣﻘﺼﻮﺩ ﺍﻹﻣﺎﻣﺔ ...

ﻭﻟﻬﺬﺍ ﻗﺎﻝ ﺃﺋﻤﺔ ﺍﻟﺴﻨﺔ : ﻣﻦ ﺻﺎﺭ ﻟﻪ ﻗﺪﺭﺓ ﻭ ﺳﻠﻄﺎﻥ ﻳﻔﻌﻞ ﺑﻬﻤﺎ ﻣﻘﺼﻮﺩ

ﺍﻟﻮﻻﻳﺔ ﻓﻬﻮ ﻣﻦ ﺃﻭﻟﻲ ﺍﻷﻣﺮ "


( ﻣﻨﻬﺎﺝ ﺍﻟﺴﻨﺔ ، ١/١٤١ )


Sannan wannan ma'anar da lafazin yake 'dauka _ har wa yau

_ tana nuni akan wajibcin biyayya ga shugaba wanda yake

'kar'kashin shugabancin Shugaba Babba wanda ya

shugabantar da shi a wani sashe na sassan jagorancin

Mutane , kamar Al'kalanci , ko limanci , ko Gwamna , ko wata

ma'aikata daga cikin ma'aikatu na Gwamnati .

Saboda làfazin " ﺗﺄﻣﺮ " yana iya 'daukan cewa : shugabane

mai

babban shugabanci ya shugabantar da Bawan a wani reshe

daga cikin rassa na jagoranci , sai Bawan ya shugabantu .


Acikin wannan akwai martani ga malaman da suka taqaita

wajibcin biyayya ga Azzalumin Shugaba ga Shugaba mai

babban shugabanci ; su ka banbanta tsakanin mai 'karamin

shugabanci da kuma mai babban shugabanci .


Rashin banbancewa tsakanin su wurin wajibcin biyayya

garesu shine abunda wannan hadisin ya tabbatar , ko dai ta

hanyar 'kiyasi ( ﺍﻟﻘﻴﺎﺱ ﺍﻷﻭﻟﻮﻱ ، ﺃﻭ ﻓﺤﻮﻯ ﺍﻟﺨﻄﺎﺏ ) a bisa

ma'anar da lafazin ya 'dauka a wannan lamba , ko kuma ta

hanyar abunda lafazin ya nuna a zahiri a bisa ma'anarsa ta

lambar da ta gabata .


Hakanan kuma Hadisin Abu Huraira yana 'kara tabbatar da

rashin banbancewa tsakanin su , inda Annabi yake cewa :


" ﻭ ﺃﻥ ﺗﻨﺎﺻﺤﻮﺍ ﻣﻦ ﻭﻻﻩ ﺗﻌﺎﻟﻰ ﺃﻣﺮﻛﻢ "


( ﻣﺴﻠﻢ : ١٧١٥ )

Anan Annabi ya yi bayanin wajibcin tsantsanta bayar da

ha'k'ki ne na shugaba a sake ( ﻋﻠﻰ ﺍﻹﻃﻼﻕ ) , bai

dabaibaye shugabancin ba da wata sifa ba sa'banin wanin ta

; ma'ana bai ce ba :

" ﻣﻦ ﻭﻻﻩ ﺗﻌﺎﻟﻰ ﺃﻣﺮﻛﻢ ﻭﻻﻳﺔ ﻋﻈﻤﻰ "

ko kuma :

" ﻭﻻﻳﺔ ﺻﻐﺮﻯ "

ko kuma :

" ﻭﻻﻳﺔ ﻋﺎﺩﻟﺔ "

ko kuma :

" ﻭﻻﻳﺔ ﺟﺎﺋﺮﺓ "

Da ya zama Annabi baki dabaibaye lafazin ba da wata sifa ba

daga cikin wa'dannan sifofi , hakan yake nuna dukkan su

suna iya shiga cikin lafazin .


Saboda haka rabewa tsakanin babban shugabanci da 'karami

wurin wajibcin biyayya ga shugaba , rabewa ne da ya

sa'bawa shari'a da lafiyayyen hankali ; domin rabewa ne

tsakanin ababe biyu da shari'a ta ha'dasu wuri guda .


Ibnu Taimiyyah yana magana akan wannan mas'alar sai yake

cewa :


" ﺇﻥ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻗﺪ ﺗﻨﺎﺯﻋﻮﺍ ﻓﻲ ﻭﻟﻲ ﺍﻷﻣﺮ ﺍﻟﻔﺎﺳﻖ ﻭ ﺍﻟﺠﺎﻫﻞ ، ﻫﻞ ﻳﻄﺎﻉ

ﻓﻴﻤﺎ ﺃﻣﺮ ﺑﻪ ﻣﻦ ﻃﺎﻋﺔ ﻭ ﻳﻨﻔﺬ ﺣﻜﻤﻪ ﻭ ﻗﺴﻤﻪ ﺇﺫﺍ ﻭﺍﻓﻖ ﺍﻟﻌﺪﻝ ، ﺃﻭ ﻻ

ﻳﻄﺎﻉ ﻓﻲ ﺷﺊ ﻭ ﻻ ﻳﻨﻔﺬ ﺷﺊ ﻣﻦ ﺣﻜﻤﻪ ﻭ ﻗﺴﻤﻪ ، ﺃﻭ ﻳﻔﺮﻕ ﻓﻲ ﺫﻟﻚ

ﺑﻴﻦ ﺍﻹﻣﺎﻡ ﺍﻷﻋﻈﻢ ﻭ ﺑﻴﻦ ﺍﻟﻘﺎﺿﻲ ﻭ ﻧﺤﻮﻩ ﻣﻦ ﺍﻟﻔﺮﻭﻉ ﻋﻠﻰ ﺛﻼﺛﺔ

ﺃﻗﻮﺍﻝ : ﺃﺿﻌﻔﻬﺎ ﻋﻨﺪ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻫﻮ ﺭﺩ ﺟﻤﻴﻊ ﺃﻣﺮﻩ ﻭ ﺣﻜﻤﻪ ﻭ ﻗﺴﻤﻪ ،

ﻭ ﺃﺻﺤﻬﺎ ﻋﻨﺪ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ ﻭ ﺃﺋﻤﺔ ﺍﻟﻔﻘﻬﺎﺀ ﻫﻮ ﺍﻟﻘﻮﻝ ﺍﻷﻭﻝ ؛ ﻭ ﻫﻮ ﺃﻥ

ﻳﻄﺎﻉ ﻓﻲ ﻃﺎﻋﺔ ﺍﻟﻠﻪ ﻣﻄﻠﻘﺎ ﻭ ﻗﺴﻤﺘﻪ ﺑﺎ ﻟﻌﺪﻝ ﻋﻠﻰ ﻫﺬﺍ ﺍﻟﻘﻮﻝ ، ﻛﻤﺎ

ﻫﻮ ﻗﻮﻝ ﺃﻛﺜﺮ ﺍﻟﻔﻘﻬﺎﺀ ، ﻭﺍﻟﻘﻮﻝ ﺍﻟﺜﺎﻟﺚ ﻫﻮ ﺍﻟﻔﺮﻕ ﺑﻴﻦ ﺍﻹﻣﺎﻡ ﺍﻷﻋﻈﻢ ﻭ

ﻏﻴﺮﻩ ، ﻷﻥ ﺫﻟﻚ ﻻ ﻳﻤﻜﻦ ﻋﺰﻟﻪ ﺇﺫﺍ ﻓﺴﻖ ﺇﻻ ﺑﻘﺘﺎﻝ ﻭ ﻓﺘﻨﺔ ، ﺑﺨﻼﻑ

ﺍﻟﺤﺎﻛﻢ ﻭ ﻧﺤﻮﻩ ، ﻓﺈﻧﻪ ﻳﻤﻜﻦ ﻋﺰﻟﻪ ﺑﺪﻭﻥ ﺫﻟﻚ ، ﻭﻫﻮ ﻓﺮﻕ ﺿﻌﻴﻒ ؛ ﻓﺈﻥ

ﺍﻟﺤﺎﻛﻢ ﺇﺫﺍ ﻭﻻﻩ ﺫﻭ ﺍﻟﺸﻮﻛﺔ ﻟﻢ ﻳﻤﻜﻦ ﻋﺰﻟﻪ ﺇﻻ ﺑﻔﺘﻨﺔ ، ﻭﻣﺘﻰ ﻛﺎﻥ

ﺍﻟﺴﻌﻲ ﻓﻲ ﻋﺰﻟﻪ ﻣﻔﺴﺪﺓ ﺃﻋﻈﻢ ﻣﻦ ﻣﻔﺴﺪﺓ ﺑﻘﺎﺋﻪ ﻟﻢ ﻳﺠﺰ ﺍﻻﺗﻴﺎﻥ

ﺑﺄﻋﻈﻢ ﺍﻟﻔﺴﺎﺩﻳﻦ ﻟﺪﻓﻊ ﺃﺩﻧﺎﻫﻤﺎ ، ﻭ ﻛﺬﻟﻚ ﺍﻹﻣﺎﻡ ﺍﻷﻋﻈﻢ ، ﻭ ﻟﻬﺬﺍ ﻛﺎﻥ

ﺍﻟﻤﺸﻬﻮﺭ ﻣﻦ ﻣﺬﻫﺐ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﺃﻧﻬﻢ ﻻ ﻳﺮﻭﻥ ﺍﻟﺨﺮﻭﺝ ﻋﻠﻰ ﺍﻷﺋﻤﺔ ﻭ

ﻗﺘﺎﻟﻬﻢ ﺑﺎﻟﺴﻴﻒ ﻭ ﺇﻥ ﻓﻴﻬﻢ ﻇﻠﻢ ، ﻛﻤﺎ ﺩﻟﺖ ﻋﻠﻰ ﺫﻟﻚ ﺍﻷﺣﺎﺩﻳﺚ

ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ ﺍﻟﻤﺴﺘﻔﻴﻀﺔ "


( ﻣﻨﻬﺎﺝ ﺍﻟﺴﻨﺔ ، ٨٦ / ٤ ‏)


6. lafazin " ﺇﻥ ﺗﺄﻣﺮ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻋﺒﺪ " , yana nuni akan cewa wajibine

biyayya ga shugaba koda kuwa Bawa ne sawu'un Bawan

Azzalumi ne ko ko Adali ne . Abunda yake tabbatar da

wannan ma'anar shine ; gamewar ma'ana da lafazin " ﻋﺒﺪ"

yake 'dauke da ita a cikin hadisin , saboda shi lafazin Surassa

sura ce ta " ﻧﻜﺮﺓ " wacce aka ambaceta abayan shara'di ;

zuwa da lafazi a irin wannan yanayi yana hukunta gamewar

hukuncin da aka tabbatar ga lafazin ga dukkan abunda yake

iya 'daukan ma'anar Sa , wannan 'ka'ida ce shahararriya a

wurin Malaman Usulul fiqh , Shehinmu yana cewa a lokacin

da yake bijiro da sigogin da suke hukunta gamewar hukunci :


" ﻭﻣﺎ ﺃﺗﻰ ﻧﻜﺮﺓ ﻓﻠﺘﻌﻠﻢ ** ﻋﻨﺪ ﺳﻴﺎﻕ ﺷﺮﻁ ﺍﻭ ﻣﺴﺘﻔﻬﻢ .


Saboda haka , zuwa da wannan lafazi a wannan yanayi yana

'kara tabbatar da fa'idar da muka gabatar a lamba ta 'daya

cewa : wajibcin biyayya ga shuwagabanni ya game dukkan

wanda yake amsa sunan Shugaba ; sawa'un Adali ne ko

Azzalumi .


7. lafazin " ﻋﺒﺪ " , lafazi ne wanda aka danganta masa wani

hukunci ( ﻣﺴﻨﺪ ﺇﻟﻴﻪ ), kuma anzo da shi a sura ta " ﻧﻜﺮﺓ " ،

hakan yana fa'idantar da bayanin wula'kantuwa da

'kas'kancin sha'anin wanda aka danganta masa wannan

hukunci . 


Ma'anar jumlar shine :


" koda ta yiwu wani wula'kantaccen Bawa 'kas'kantacce ya

shugabantu akanku ,to Ku yi masa biyayya "

a larabce sai jumlar ta zama :


" ﻭ ﺇﻥ ﺗﺄﻣﺮ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻋﺒﺪ ﻣﺴﺘﺤﻘﺮ ﻣﻬﺎﻥ ﻓﺎﺳﻤﻌﻮﺍ ﻭ ﺃﻃﻴﻌﻮﻩ "


Wannan fa'idar tana daga cikin fa'idojin da Suna ( ﺍﻻﺳﻢ )

Nakirah ( ﺍﻟﻨﻜﺮﺓ ) yake 'dauka idan aka zo dashi a matsayin

wanda aka jingina masa wani hukunci .

Ibnu Shihna Alhalaby yana cewa akan wannan batu :


" ﻭ ﺇﻥ ﻣﻨﻜﺮ ﻓﻠﻠﺘﺤﻘﻴﺮ * * ﻭ ﺍﻟﻀﺪ ﻭ ﺍﻹﻓﺮﺍﺩ ﻭ ﺍﻟﺘﻜﺜﻴﺮ .


Bayanin wannan ma'anar da lafazin ya 'dauka , ya zo 'karara

a wasu riwayoyi ; inda Annabi ya fayyace 'karara cewa koda

Bawan wula'kantacce ne mara daraja , to wajibine a yi masa

biyayya , Hadisin Al'imam Muslim na Ummul Hasin ya

fayyace haka a fili , Annabi yake cewa :


" ﺍﺳﻤﻌﻮﺍ ﻭ ﺃﻃﻴﻌﻮﺍ ﻭ ﺇﻥ ﺃﻣﺮ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻋﺒﺪ ﺣﺒﺸﻲ ﻣﺠﺪﻉ "


Anan Annabi ya bayyana cewa koda Bawan da shugabantu

akan mutane wula'kantacce ne ; ta yanda ya zama Ba'kin

Bawa ne , mai katsatstsen Hanci , wanda kuma duk Bawan

da yà zama a irin wannan sifa to babu shakka wula'kantacce

ne mara 'kima a wurin mutane . Amma duk da irin wannan

yanayi da ya kiwaye shugabancin Sa , Annabi bai saryar da

wajibcin biyayya gareshi ba .


8. Manzan Allah ya rattaba wasu irin yanayi _ marasa da'di _

akan shugabancin wani shugaba , ta hanyar ambaton cewa

koda shugabanci yana tattare da ababe kamar haka :


* Shugaban wula'kantaccen Bawa ne _ gashi kuma Bawa da

shi da dukiyar Sa Mallakan Ubangidansa ne _ amma kuma a

wayi gari a ce shine al'umma za su runsunamawa !!


* Koda Bawan ba Adali bane , kuma 'kwatan Mulkin ya yi da

'karfin Makami ; ya zama shugaba a bisa 'barauniyar hanya

wacce mutane suke inkarinta !!


* koda Bawan 'dorashi aka yi akan mutane , alhalin basa

'kaunassa a matsayin shugaba garesu .

Duk da irin wannan yanayi _abun 'kyama _ , da suka kewaye

wannan shughabanci , Manzan Allah bai saryar da wajibcin

biyayya ba ga shugaban , a'a sai ya wajabta biyayya gareshi

domin kiyaye maslaha mafi rinjaye na Addinin mutane da

rayuwarsu da zaman lafiyar su .

Wannan yana nuna shugaban da yake a sa'banin wa'dannan

miyagun sifofi shi ya fi cancanta da ayi masa biyayya Sama

da wanda yake akan irin wa'dannan miyagun sifofi . Kenan

anan Annabi ya fa'dakar da mutane ne akan mafi

wula'kantuwar al'amari zuwa ga mafi 'daukaka ( ﺍﻟﺘﻨﺒﻴﻪ ﺑﺎﻷﺩﻧﻰ

ﺇﻟﻰ ﺍﻷﻋﻠﻰ )


Kamar fa'din Allah ma'dauki :


" ﻓﻤﻦ ﻳﻌﻤﻞ ﻣﺜﻘﺎﻝ ﺫﺭﺓ ﺧﻴﺮﺍ ﻳﺮﻩ "


Wannan Ayar tana nuni akan cewa ; idan ya zama wanda ya

yi aiki daidai da qwayar zarra zai ga sakamakon sa , to

wanda ya yi manyan ayyuka shi ya fi cancanta da ya ga

sakamakon manyan ayyukansa . 


9. Lafazin " ﻭ ﺇﻥ ﺗﺄﻣﺮ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻋﺒﺪ " , jumlace ta shara'di , wacce

take bu'katuwa zuwa ga sakamakon shara'din domin

ma'anarta ta cika , amma anan an share sakamakon

shara'din _bisa wajibi _ saboda an gabatar da lafazin da yake

nuni akan ma'anarsa , wannan lafazin shine " ﻭﺍﻟﺴﻤﻊ ﻭ ﺍﻟﻄﺎﻋﺔ

" . 


Wato yanda jumlar take a asàli shine :


" ﻭﺍﻟﺴﻤﻊ ﻭ ﺍﻟﻄﺎﻋﺔ ، ﻭ ﺇﻥ ﺗﺄﻣﺮ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻋﺒﺪ ﻓﺎﺳﻤﻌﻮﺍ ﻭ ﺃﻃﻴﻌﻮﺍ "


To amma an wadatu da jumlar shara'din daga rashin ambaton

sakamakon shara'din saboda an gabatar da lafazin da yake

nuni akan ma'anarsa .

Zuwan sakamakon shara'di a irin wannan yanayi yana

wajabta rashin ambaton Sa da wadatuwa da jumlar shara'di ,

misali akan haka fa'din Allah ma'daukaki :


" ﻭ ﺧﺎﻓﻮﻥ ﺇﻥ ﻛﻨﺘﻢ ﻣﺆﻣﻨﻴﻦ "


Ta'kadirin jumlar shine :


" ﻭ ﺧﺎﻓﻮﻥ ﺇﻥ ﻛﻨﺘﻢ ﻣﺆﻣﻨﻴﻦ ﻓﺨﺎﻓﻮﻧﻲ "


Amma an goge sakamakon shara'din saboda an gabatar da

lafazin da yake nuni akan ma'anar Sa .


Ibnu Malik ya ce :


" ﻭ ﺍﻟﺸﺮﻁ ﻳﻐﻨﻲ ﻋﻦ ﺟﻮﺍﺏ ﻗﺪ ﻋﻠﻢ ** ﻭ ﺍﻟﻌﻜﺲ ﻳﺄﺗﻲ ان المعنى فهم

"

Saboda haka , ga'ba ta farko na hadisin :


" ﺃﻭﺻﻴﻜﻢ ﺑﺘﻘﻮﻯ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﺰ ﻭ ﺟﻞ ، ﻭ ﺍﻟﺴﻤﻊ ﻭ ﺍﻟﻄﺎﻋﺔ "


Wannan ga'bar tana wajabta biyayya ga ko wane irin shugaba

ne a dun'kule ; hakan ya 'kunshi Adali da Azzalumi , 'Da ko

Bawa .


Ga'ba ta biyu kuma :

" ﻭ ﺇﻥ ﺗﺄﻣﺮ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻋﺒﺪ "

Tana 'kara 'karfafa wajibcin wannan biyayyar koda kuwa

shugabancin ya samu ne ta haramtacciyar hanya .


10 . Wannan umurni da Annabi ya yi na wajibcin biyayya ga

shuwagabanni a bisa yanayin da suke _ kamar yanda muka

fahimta daga lafuzzan hadisin _ , yana nuni akan haramcin

tawaye garesu komin munin halinsu , kuma a bisa ko wace

irin hanya suka haye madafan iko .

Kamar yanda yake sananne a ilimin usulul fiqh cewa; umurni

da wani abu hani ne gameda kishiyar wanabun ( ﺍﻷﻣﺮ ﺑﺎﻟﺸﺊ

ﻧﻬﻲ ﻋﻦ ﺿﺪﻩ ) .


Saboda haka , umurni da aka yi da biyayya ga shugaba yana

lazimta haramcin tawaye gareshi ;saboda tawayen yana

warware biyayya ta wajibine gareshi , saboda haka, tawayen

haramun ne .


Manzan Allah ya ha'da abubuwan guda biyu a wuri 'daya _

domin qarfafa wajibcin biyayya ga shugaba da haramcin

tawaye gareshi _ a cikin hadisin Ubadah bin Samit , Ubadah

ya ce :


" ﺑﺎﻳﻌﻨﺎ ‏( ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ‏) : ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺴﻤﻊ ﻭ ﺍﻟﻄﺎﻋﺔ ﻓﻲ ﻣﻨﺸﻄﻨﺎ ﻭ ﻣﻜﺮﻫﻨﺎ ﻭ

ﻋﺴﺮﻧﺎ ﻭ ﻳﺴﺮﻧﺎ ، ﻭ ﺃﺛﺮﺓ ﻋﻠﻴﻨﺎ ، ﻭ ﺃﻥ ﻻ ﻧﻨﺎﺯﻉ ﺍﻷﻣﺮ ﺃﻫﻠﻪ "...

‏( ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ : ٧٠٥٦ )


Anan da Annabi ya umurci Sahabbai da Biyayya ga

shuwagabanni _ wanda hakan yana lazimta rashin tawaye

garesu _ , Amma sai bai wadatu da hakan ba domin ya

'karfafa musu Wannan umurni, kuma ya fayyace musu 'karara

cewa baya halatta su sa'bawa Wannan umurni ta hanyar

tawaye ga shuwagabanni , sai ya 'kara musu da cewa :


" ﻻ ﺗﻨﺎﺯﻋﻮﺍ ﺍﻷﻣﺮ ﺃﻫﻠﻪ "


Ma'ana : kar Ku yi fito_na _fito da Shuwagabanni domin

'kwace mulkin su .


Ibnu Taimiyyah yana bayanin ma'anar Wannan lafazin sai

yake cewa :


" ﻭ ﻧﻬﻰ ‏( ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ‏) ﻋﻦ ﻣﻨﺎﺯﻋﺔ ﺍﻷﻣﺮ ﺃﻫﻠﻪ ، ﻭ ﺫﻟﻚ ﻧﻬﻲ ﻋﻦ

ﺍﻟﺨﺮﻭﺝ ﻋﻠﻴﻪ ، ﻷﻥ ﺃﻫﻠﻪ ﻫﻢ ﺃﻭﻟﻮ ﺍﻷﻣﺮ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﺃﻣﺮ ﺑﻄﺎﻋﺘﻬﻢ ، ﻭﻫﻢ

ﺍﻟﺬﻳﻦ ﻟﻬﻢ ﺳﻠﻄﺎﻥ ﻳﺄﻣﺮﻭﻥ ﺑﻪ ، ﻭﻟﻴﺲ ﺍﻟﻤﺮﺍﺩ ﻣﻦ ﻳﺴﺘﺤﻖ ﺃﻥ ﻳﻮﻟﻰ ﻭﻻ

ﺳﻠﻄﺎﻥ ﻟﻪ ، ﻭﻻ ﺍﻟﻤﺘﻮﻟﻲ ﺍﻟﻌﺎﺩﻝ ، ﻓﺈﻧﻪ ﻗﺪ ﺫﻛﺮ ﺃﻧﻬﻢ ﻳﺴﺘﺄﺛﺮﻭﻥ ، ﻓﺪﻝ

ﻋﻠﻰ ﺃﻧﻪ ﻧﻬﻰ ﻋﻦ ﻣﻨﺎﺯﻋﺔ ﻭﻟﻲ ﺍﻷﻣﺮ ﻭ ﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﻣﺴﺘﺄﺛﺮﺍ "


‏( ﻣﻨﻬﺎﺝ ﺍﻟﺴﻨﺔ ، ٤ / ٨٨ )


Saboda haka ,wannan Hadisin yana nuni akan haramcin

tawaye ga Azzaluman Shuwagabanni , kuma akan haka

mazhabar Ahlussunnah ta gudana , wa'danda suka sa'bawa

musu akan haka sune 'kungiyoyi 'yan narko ( ﺍﻟﻮﻋﻴﺪﻳﺔ ) ;

KKhawarij da mu'tazila da Shi'a Rafidha .

Shaikhul Islam ya ce :


" ﺍﺳﺘﻘﺮ ﺃﻣﺮ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻋﻠﻰ ﺗﺮﻙ ﺍﻟﻘﺘﺎﻝ ﻓﻲ ﺍﻟﻔﺘﻨﺔ ﻟﻸﺣﺎﺩﻳﺚ

ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ ﺍﻟﺜﺎﺑﺘﺔ ﻋﻦ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭ ﺳﻠﻢ ، ﻭ ﺻﺎﺭﻭﺍ ﻳﺬﻛﺮﻭﻥ

ﻫﺬﺍ ﻓﻲ ﻋﻘﺎﺋﺪﻫﻢ ﻭ ﻳﺄﻣﺮﻭﻥ ﺑﺎ ﻟﺼﺒﺮ ﻋﻠﻰ ﺟﻮﺭ ﺍﻷﺋﻤﺔ ﻭ ﺗﺮﻙ ﻗﺘﺎﻟﻬﻢ ،

ﻭﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﻗﺪ ﻗﺎﺗﻞ ﻓﻲ ﺍﻟﻔﺘﻨﺔ ﺧﻠﻖ ﻛﺜﻴﺮ ﻣﻦ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻭ ﺍﻟﺪﻳﻦ "


‏( ﻣﻨﻬﺎﺝ ﺍﻟﺴﻨﺔ ، ٤ / ٢٤١ ‏)


11. Acikin wannan Hadisi akwai tabbatar da 'ka'idar " ﺍﺭﺗﻜﺎﺏ

ﺃﺧﻒ ﺍﻟﻀﺮﺭﻳﻦ " , ta yanda Annabi ya yi umurni akan ha'kuri da

wanzuwa 'kar'kashin jagorancin wanda bai cancanci

jagorancin ba ; sai aka ha'kura da aikata ''karamar 'barna ta

hanyar gujewa 'barnar da ta 'daranmata ; Wannan 'barnar

kuwa itace tawaye garesu .


12. Biyayya ga shuwagabanni al'amari ne mai muhimmanci a

shari'a , shi yasa Annabi ya yi nuni zuwa ga haka acikin

wannan Hadisin ta hanyar ambaton hakan a dunqule a farkon

saqonsa ; inda ya ce :


ﺃﻭﺻﻴﻜﻢ ﺑﺘﻘﻮﻯ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﺰ ﻭﺟﻞ "


Babu shakka biyayya ga shuwagabanni yana daga cikin

kiyaye dokokin Allah da Annabi ya yi umurni da shi , amma

kuma sai Annabi ya sake ambaton wajibcin biyayya ga

shuwagabannin 'karara a ke'be , domin ya bayyana girman

muhimmancin hakan a musulunci , kuma ya tabbatar da cewa

lallai hakan yana daga cikin kiyaye dokokin Allah .


Irin Wannan salo na zance shine Malaman Balaga suke ce

dashi :" ﺍﻹﻃﻨﺎﺏ " .


13. Kamar yanda tawaye ga Azzalumin Shugaba yake

haramun , to hakanan duk abunda zai iya zama kafa zuwa ga

Samar da wannan tawaye to shima haramun ne , kamar

yanda yake hakan 'ka'ida ce tabbatacciya acikin shari'a


.Malamai suna cewa :


" ﻛﻞ ﻣﺎ ﻳﻜﻮﻥ ﺫﺭﻳﻌﺔ ﺇﻟﻰ ﻣﺤﺮﻡ ﻓﻬﻮ ﻣﺤﺮﻡ "


Shaikhul Islam ya ce :


" ﻭﺍﻟﻔﻌﻞ ﺇﺫﺍ ﻛﺎﻥ ﻳﻔﻀﻲ ﺇﻟﻰ ﻣﻔﺴﺪﺓ ﻭ ﻟﻴﺲ ﻓﻴﻪ ﻣصلحة ﺭﺍﺟﺤﺔ ﻳﻨﻬﻰ

ﻋﻨﻪ "


‏( ﻗﺎﻋﺪﺓ ﺟﻠﻴﻠﺔ ﻓﻲ ﺍﻟﺘﻮﺳﻞ ﻭ ﺍﻟﻮﺳﻴﻠﺔ ، ٤٦ )


Saboda haka , Samar da wasu Qungiyoyi masu fafutuka akan

hayewa madafan iko bayan samuwan shugaba ; wadanda

zasu zama 'Yan Hamayya ga shugaban , Wannan ya sa'bawa

tsari na musulunci .


Hakanan bayyana inkari ga shugaba abainar jama'a shima

haramun ne ; saboda kafa ce zuwa ga tawaye gareshi .


Shi yasa Annabi ya fito 'karara ya hana gyàrawa Shugaba

kuskuren Sa ta Wannan fuskar ; ya taqaita hanyar gyaran_

kawai _ ta hanyar ke'bewa da shugaban .


Ibnu Abi Asim ya ruwaito da tabbataccen isnadin Sa , daga

Sahabi Iyadh bin Ganam , ya ce Annabi ya ce :


" " ﻣﻦ ﺃﺭﺍﺩ ﺃﻥ ﻳﻨﺼﺢ ﻟﺬﻱ ﺳﻠﻄﺎﻥ ﻓﻼ ﻳﺒﺪﻩ ﻋﻼﻧﻴﺔ ، ﻭﻟﻜﻦ ﻳﺄﺧﺬ ﺑﻴﺪﻩ

ﻓﻴﺨﻠﻮ ﺑﻪ ، ﻓﺈﻥ ﻗﺒﻞ ﻣﻨﻪ ﻓﺬﺍﻙ ، ﻭ ﺇﻻ ﻛﺎﻥ ﻗﺪ ﺃﺩﻯ ﺍﻟﺬﻱ ﻋﻠﻴﻪ "


‏( ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻻﺑﻦ ﺃﺑﻲ ﻋﺎﺻﻢ ، ٥٢١ )


Cewa da Annabi ya yi " ﻟﺬﻱ ﺳﻠﻄﺎﻥ " , yana nuni akan

haramcin

bayyana inkarin ga ko wane irin Shugabancin Mutumin yake

dashi ; ma'ana shugabanci ne baba ko 'karami , shugabanci

ne na daular musulunci , ko ko shugabancin ba na musulunci

bane .


Dalili akan haka shine : Annabi ya fa'di lafazin ne a sake "


ﻋﻠﻰ ﺍﻻﻃﻼﻕ " , saboda haka ko wane irin shugabanci zai shiga

cikin lafazin Hadisin , duk wanda ya fito ya ce : banda irin

shugabanci Kaza " , to za'a neme shi da ya Kawo dalilinsa na

dabaibaye lafazin Hadisin da wata sifa da Annabi bai bayyana

ta ba ga Wannan lafazin.


Acikin haka akwai martani ga masu cewa : wai shugabanni

bisa shugabanci na demokra'diyya ya halatta a caccake su a

bayyana inkari garesu abayyana inkari garesu a bainar jama'a

, suka ce wai Annabi shuwagabanni na musulunci yake nufi !!

babu shakka Wannan yi wa Maganar Annabi dabaibayi ne da

abunda bai mata dabaibayi da shi ba , yin hakan kuma ba

haqqi ne na wani mahaluqi ba , a'a haqqi ne na Annabi ,

tunda kuma shi bai yi ba , to babu wanda ya Isa ya yi hakan

kuma a kar'bi hakan daga gareshi !!


Hakanan cewa da Annabi ya yi :" ﺃﻥ ﻳﻨﺼﺢ " ,shima lafazi ne

sakakke ( ﻣﻄﻠﻖ ) , saboda haka nasihar ta shafi ko wane

kuskure ne yake aikatawa; kuskure ne da cutarwassa ya

ta'kaita akan Kansa shi ka'dai , ko ko a'a kuskuren

cutarwassa ya shafi al'ummar da yake jogaoranta , ko kuma

kuskure ne da yake aikatawa a bayyane , ko kuma kuskure na

'boye ; dukkan wa'dannan nau'uka na kurakurai na shugaba

zasu shiga cikin lafazin hadisin .

Saboda haka , duk wanda ya

ware wani nau'i na kuskure ya ce ya halatta

a bayyana inkari akan shugaba akan Sa , to za'a nemeshi da

ya Kawo dalilin ware Wannan Surar da halasci .


Sahababn Annabi sun gudana akan tabbatar da abunda

Wannan HADISI yake nunawa ; na ke'bewa da shugaba yayin

nasiha gareshi .


Wasu mutane sun sami Usama bin zaid, sai

suka neme shi da ya yiwa Khalifah nasiha akan sha'anin

jagorancinsa , sai Usama ya ce da su :


" ﻗﺪ ﻛﻠﻤﺘﻪ ﻣﺎ ﺩﻭﻥ ﺃﻥ ﺃﻓﺘﺢ ﺑﺎﺑﺎ ﺃﻛﻮﻥ ﺃﻭﻝ ﻣﻦ ﻳﻔﺘﺤﻪ "


( ﺑﺨﺎﺭﻱ : ٧٠٩٨ )


Anan sai Usama ya fa'da musu cewa ; ya yi masa

nasiha akan matsalar , Amma a 'boye ya yi masanasihar ; bai

bayyana nasihar a bainar jama'à ba domin kar ya zama yazo

da wata sabuwar Bid'a ta bayyana inkari ga shugaba a bainar

jama'a ,wanda babu wanda ya gabaceshi akan haka . Saboda

haka , haramun ne bayyana inkari ga shugaba .


Ibnu Hajar ya ce gameda wannan Hadisi :


" ﻗﺎﻝ المهلب : ﻗﺎﻝ ﺃﺳﺎﻣﺔ : " ﻗﺪ ﻛﻠﻤﺘﻪ ﺳﺮﺍ ﺩﻭﻥ ﺃﻥ ﺃﻓﺘﺢ ﺑﺎﺑﺎ ، ﺃﻱ

ﺑﺎﺏ

ﺍﻟﭑﻧﻜﺎﺭ ﻋﻠﻰ ﺍﻷﺋﻤﺔ ﻋﻼﻧﻴﺔ ﺧﺸﻴﺔ ﺃﻥ ﺗﻔﺘﺮﻕ ﺍﻟﻜﻠﻤﺔ "

ﻭ ﻗﺎﻝ ﻋﻴﺎﺽ :


" ﻣﺮﺍﺩ ﺃﺳﺎﻣﺔ ﺃﻧﻪ ﻻ ﻳﻔﺘﺢ ﺑﺎﺏ ﺍﻟﻤﺠﺎﻫﺮﺓ ﺑﺎ ﻟﻨﻜﻴﺮ ﻋﻠﻰ ﺍﻹﻣﺎﻡ ﻟﻤﺎ

ﻳﺨﺸﻰ ﻣﻦ ﻋﺎﻗﺒﺔ ﺫﻟﻚ ﺑﻞ ﻳﺘﻠﻄﻒ ﺑﻪ ﻭ ﻳﻨﺼﺤﻪ ﺳﺮﺍ ﻓﺬﻟﻚ ﺃﺟﺪﺭ ﺑﺎ

ﻟﻘﺒﻮﻝ "


( ﻓﺘﺢ ﺍﻟﺒﺎﺭﻱ ، ١٣ /٤٤ )


maganar kuma cewa ai wani Malami , ko wani Sahabi ya yi ,

Wannan duk ba Hujja bane , Hujja itace maganar Allah ko ta

Annabi , amma wani mutum _ko wanene _ aikinsa ba Hujja

bane a addini , balle kuma idan Aikin nasa ma ya ci karo da

maganar Allah ko ta Annabi !!.


 Abunda za'a iya cewa a Wannan yanayi shine : a bawa

Wannan malamin uzuri da cewa ; ya yi ri'ko ne da dalilai

gamammu da suke umurni da inkari ga wanda ya sa'bawa

shari'a kai tsaye , sai malamin ya gafala da dalilin da ya

ke'be shugaba da rashin bayyana hakan gareshi a bainar

jama'a .


ko kuma a ce malamin yana ganin maslahar bayyana inkarin

a wannan yanayi yafi rinjaye

Sama da rashin haka , ko kuma ma zata yiwu in ba a wannan

yanayin ba gusar da ''barnar ba zata yiwu ba . saboda haka

sai malamin ya ribaci Wannan yanayin domin ya cimma

maslaha mafi rinjaye . Sanannen

abune a shari'a cewa dukkan

abunda aka haramtashi Saboda zamantowarsa kafa ne zuwa

ga abunda yake haramun ,to ana halasta shi saboda

wata maslaha mafi rinjaye . 

Shaikhul Islam ya ce:


" ﺍﻟﻨﻬﻲ ﺇﺫﺍ ﻛﺎﻥ ﻟﺴﺪ ﺫﺭﻳﻌﺔ ﺃﺑﻴﺢ ﻟﻤﺼﻠﺤﺔ ﺭﺍﺟﺤﺔ "


‏( ﻗﺎﻋﺪﺓ ﺟﻠﻴﻠﺔ ، ٤٦ )


Saboda

haka , Wannan yana daga abunda za'a iya cewa

gameda

irin Wannan yanayi , amma bai yiwuwa a yi watsi da Hadisi

_wai_Saboda ya

sa'bawa aikin wani mutum , ko kuma a ce za'a yi jam'i

tsakanin Hadisin Annabi da aikin wani malami da ya sa'bawa hadisi , wannan duka kuskure ne ; ba'a yin jam'i tsakanin abunda yake Hujja da wanda ba Hujja ba ; ana jam'i net sakanin dalili da dalili . Al'imam Ashshaukany ya ce :

" ﺇﻧﻤﺎ ﻳﻘﺘﺪﻱ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﺑﺄﻫﻞ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻓﻲ ﺍﻟﺨﻴﺮ ، ﻓﺈﻥ ﺟﺎﺅﻭﺑﻤﺎ ﻳﺨﺎﻟﻒ

ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭ ﺍﻟﺴﻨﺔ ، ﻓﺎﻟﻘﺪﻭﺓ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ ﻣﻊ ﺇﺣﺴﺎﻥ ﺍﻟﻈﻦ ﺑﻬﻢ ، ﻭ

ﺣﻤﻠﻬﻢ ﻋﻠﻰ ﻣﺤﺎﻣﻞ ﺣﺴﻨﺔ ﻣﻘﺒﻮﻟﺔ "

( ﺍﻟﻔﺘﺢ ﺍﻟﺮﺑﺎﻧﻲ ، ٥٥٩٣ )



 
Follow Admin On Twitter Ibrahim Yunusa Abu-ammar
Subscribed Our Newsletter